25 Maris 2021 - 13:36
Niger: Majiyar Jami’an Tsaron Kasar Ta Bada Labarin Mutuwar Akalla Mutane 10 A wani harin Ta’addanci A Kudancin kasar

Akalla mutane 10 ne jami’an tsaro a jumhuriyar Niger suka bada sanarwan mutuwarsu sanadiyyar hare-haren da ‘yan bindiga suka kai kan wasu kauyuka biyu a yankin Telleberi na kudu maso yammacin kasar.

ABNA24 : Majiyar ta kara da cewa ‘yan bindigan sun kar hari a kauyen Zibane inda suka kashe mutane 3 sannan a kauyen Gabado kuma suka kashe mutane 7. Banda haka sun kona wasu makarantu a kauyukan.

A ranar lahadin da ta gabata ma ‘yan bindiga sun kashe mutane 137 a yankin, wanda shini mafi muni da suka kai a cikin ‘yan shekarun da ska gabata.

Gwamnatin kasar tana tuhumar kungiyoyin ‘yan ta’adda masu riya kishin addini a yankin. Amma har yanzun ba wanda ya dauki alhakin kissan har yanzun.

342/